Kasuwanci

  • Autor: Vários
  • Narrador: Vários
  • Editor: Podcast
  • Duración: 3:54:59
  • Mas informaciones

Informações:

Sinopsis

Shirin yakan diba kasuwancida tattalin arizikin kasashen duniya ya ke ciki. Shirin yakan ji sabbin dubaru da hajojin ci gaban tattalin arzikin na kasashen duniya. Tare da jin ta bakin 'Yan kasuwa da Masanaantu dangane da halin da suke ciki.

Episodios

  • Gwamnatin Najeriya ta fara yunkurin farfaɗo da masaƙun da suka durƙushe

    13/08/2025 Duración: 09min

    Shirin Kasuwa Akai Miki Dole a wannan makon, ya mayar da hankali ne kan yunkurin da gwamnatin Najeriya Ke yi na ganin ta farfado da tattalin arzikinta, ta hanyar tada masana'antun da suka durƙushe.  Ƙaramin ministan kasuwanci na ƙasar Sanata John Owan  Enoh ya fara ziyarar wasu daga cikin masakun da suka durƙushe domin ganin sun dawo bakin aiki. Masaka ta UNTL da Ke Kaduna na cikin masakun da ministan ya ziyarta bisa ganin irin gudummuwar da ta ke bayar wa a baya. Ku latsa alamar sauti don saurorin cikakken shirin tare da Ahmed Abba............

  • Takardar kuɗin Najeriya ta samu tagomashi a kwanakinnan

    23/07/2025 Duración: 10min

    To kamar yadda akaji a matashiyar shirin, ra’ayoyin masana tattalin arziki sun banbanta a Najeriya, tun bayan da sananne a harkar tattalin arziki Bismark Rewane ya tabbatar cewa Naira ta daidaita tsakanin 1500 zuwa 1560 kan kowace dala a makonnin baya-bayan nan, yayin da tattalin arzikin ƙasar kuwa ya fara farfadowa sakamakon matakin babban bankin na Najeriya CBN da ya sanya zunzurutun ƙudi har dalar Amurka biliyan 4 da miliyan 100 cikin watanni shida na wannan shekara...ta 2025.

  • Tasirin sabuwar dokar harajin da Tinubu ya sanyawa hannu ga ƴan Najeriya

    09/07/2025 Duración: 09min

    Shirin Kasuwa a Kai Miki Dole na wannan mako tare da Ahmed Abba ya yi dubi ne kan sabuwar dokar Harajin da shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya sanya wa hannu a ƙarshen watan Yunin wannan shekara ta 2025 a matsayin wata sabuwar dokar haraji da za ta taimaka wajen sake yi wa tsarin tattara harajin ƙasar garambawul kamar yadda su ka bayyana.  Sabuwar dokar ta kuma yi bayani dalla-dalla kan waɗanda za ta shafa tare da cire wasu nau'ukan ƴan Najeriya kama daga ƴan kasuwa da ma'aikata da ma manya da matsakaitan kamfanoni. Kuma domin sanin waɗanda da dokar ta bada damar karɓar haraji a wurinsu da ma waɗanda ta ce a ɗage musu tare da irin tasirin da za ta yi ga tattalin arziƙin ƙasar. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.

página 2 de 2