Kasuwanci

Najeriya ta yi asarar sama da naira triliyan 5 a zanga-zangar kwanaki 10

Informações:

Sinopsis

Shirin Kasuwa A kai miki Dole na wannan makon tare da Ahmad Abba ya tattauna irin asarar da aka yi a Najeriya sakamakon zanga zangar kwanaki 10 da ƴan ƙasar suka yi domin nuna adawa da tsadar rayuwa da rashin shugabanci na gari. Ministar masana’antu da Kasuwanci da kuma zuba jari na kasar Dr. Doris Uzoka Anite ta ce, alkakuma da suka tattara na wucin gadi, sun nuna cewa Najeriya ta yi asarar naira biliyan 500 a duk rana ta Allah yayin zanga-zangar, bayaga dukiyar da aka barnata ta hanyar kone-kone ko sata da makamanci hakan da takai naira biliyan 52, kamar yadda ta wallafa a shafinta na X.