Bakonmu A Yau

Gwamnatin jihar Borno ta bukaci al'umar birnin Maiduguri dasu kiyaye abinda zasu ci ko su sha

Informações:

Sinopsis

Gwamnatin Jihar Barno da ke Najeriya ta gargadi mazauna birnin Maiduguri da su kaucewa cin kayan abinci da ruwan shan da aka dauko daga yankunan da aka samu ambaliya, domin samun kariya. Hukumomin sun ce wadannan kayayyaki na dauke da sinadarin dake fita daga gawarwaki da masai da wasu na dabam da ka iya haifar da cututtuka. Dangane da wannan gargadi Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Balarabe Sani Garko na Jmai'ar Ahmadu Bello dake Zaria,kuma ga yadda zantawarsu ta gudana. Sai a latsa alamar sauti damin samun cikakken shirin.