Bakonmu A Yau

Dr Aliyu Dala kan ambaliyar da ta mamaye akasarin birnin Maiduguri

Informações:

Sinopsis

Wani masani ɗan jihar Bornon Najeriya Dr Aliyu Dala ya danganta ambaliyar da ta mamaye akasarin birnin Maiduguri da sakacin jami'an gwamnati. Dr Dala wanda ke cikin ƙungiyar ƙwararrun ƴan Arewacin Najeriya mazauna Turai ya ce sun yi nazari akan matsalar ambaliyar kuma sun gabatar da rahoto a kan matakan da ya dace a dauka, cikin su harda na Maiduguri amma babu abinda aka yi a kai. Ku latsa alamar sauti don jin yadda tattaunawarsu ta gudana da Bashir Ibrahim Idris.....