Bakonmu A Yau

  • Autor: Vários
  • Narrador: Vários
  • Editor: Podcast
  • Duración: 1:18:03
  • Mas informaciones

Informações:

Sinopsis

A kullum mukan gayyaci masana a fannoni daban daban domin tattauna wasu muhimman al'amurra da suka shafi kanun labarai a duniya. wani lokacin kuma wasu manyan jami'an gwamnati da masu fada aji sukan kawo muna ziyara domin tattauna batutuwan da suka shafi matsalolin da suka shafe su ko kuma ci gaban kasa.

Episodios

  • Dr Bashir Nuhu Mabai kan janyewar Isra'ila a tattaunawarta da Hamas

    03/03/2025 Duración: 03min

    Tattaunawa tsakanin wakilan Isra'ila dana Hamas domin amincewa da shiga rukuni na biyu na yarjejeniyar tsagaita wutar da ke tsakaninsu ta katse a birnin Alqahira na Masar bayan gaza cimma daidaito. Tuni Isra'ila ta dakatar da shigar da kayakin agaji zuwa yankin Gaza da ƙungiyoyi ke jagorantar kaiwa wanda aka tattara daga ƙasashen Larabawa ga Falasɗinawan yankin da ya yi fama da yaƙin kusan shekaru 2, lamarin da ke da nasaba da yadda Hamas ta ƙi amincewa da ƙara wa'adin rukunin farko na yarjejeniyar a gefe guda Isra'ila ta ƙi amincewa da shiga rukuni na biyu, wanda ya sanya tuni Isra'ilan ta fara dawo da hare-hare zuwa wasu yankuna ciki har da Rafah.Dangane da wannan matsala Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Bashir Nuhu Mabai na jami'ar Dutsinma ga kuma yadda zantawarsu ta gudana.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

  • Farfesa Mansur Yelwa kan muhimmancin azumin watan Ramadan ga Musulmai

    28/02/2025 Duración: 03min

    Gobe Asabar ke zama 1 ga watan Ramadan na shekarar 1446 dai-dai da 1 ga watan Fabrairun 2025, abinda ke nufin al'ummar musulmi a faɗin duniya za su fara da gudanar da ibadar azumi, wanda ake gudanarwa duk shekara. A lokacin watan Ramadan al'ummar musulmi kan ruɓanya ayyukan ibadar da suke gudanarwa, domin neman dace wa a wurin Allah SWT, tare da samun falala mai tarin yawa.Kan hakan ne Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Mansur Isa Yelwa fitaccen malamin addinin musulinci a Najeriya.Latsa alamar sauti domin sauraren tattaunawar...

  • Alhaji Shu'aibu Idris kan rage farashin mai da matatar Dangote ta yi

    27/02/2025 Duración: 03min

    A yayin da ake gab da fara azumin Ramadan, Matatar Mai ta Ɗangote da ke Najeriya ta sanar da rage farashin litar man fetur da take sayar wa ƴan kasuwa daga Naira 890 zuwa Naira 825, rahusar da ta fara aiki daga yau Alhamis, 27 ga watan Fabairu. Kan hakan ne Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Alhaji Shu'aibu Idris.Latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar hirar...

página 2 de 2
Únete Ahora

Únete Ahora

  • Acceso ilimitado a todo el contenido de la plataforma.
  • Más de 30 mil títulos, incluidos audiolibros, podcasts, series y documentales.
  • Narración de audiolibros por profesionales, incluidos actores, locutores e incluso los propios autores.
Prueba ahora Firma sin compromiso. Cancele cuando quiera.

Compartir