Ilimi Hasken Rayuwa
- Autor: Vários
- Narrador: Vários
- Editor: Podcast
- Duración: 3:58:14
- Mas informaciones
Informações:
Sinopsis
Wannan Shirin ya shafi Fadakar da al'umma game da ci gaban da aka samu a sha'anin Ilimi a fannoni daban-dabam a duniya, tare da nazari ga irin ci gaban da aka cim ma wajen binciken kimiya da fasaha da ke naman saukakawa Danadam wajen tafiyar da rayuwarsa a duniya. Shirin kuma zai yi kokarin jin irin bincike da masana ke yi domin inganta rayuwar Biladam. Shirin na zo maku ne, a duk ranar Talata a shirye-shiryenmu na safe.
Episodios
-
Gwamnatin Neja na shirin farfado da tsarin karatun makiyaya
19/12/2023 Duración: 09minShirin 'Ilimi Hasken Rayuwa' na wannan makon zai yi duba ne da tsarin karatun 'yayan makiyaya, wato Nomadic Education. Gwamnatin jihar Neja ce ta yi hobbasa don farfado da shirin karatun 'yayan makiyaya a jihar. Shirin zai bai wa makiyaya damar samun ilimi a duk inda suka yi balaguro don inganta makomarsu. Yanzu haka dai shirye-shirye sun yyi nisa a game dfdaa wannan shirin a jihar Neja mai fara da matsalar tsaro sakamakon ayyukan 'yan bindiga da ke kashe mutane da satar su don kudin fansa.
-
Taimakon da kirkirarren Tabarau ke bai wa masu fama da matsalar raunin gani
28/11/2023 Duración: 10minShirin 'Ilimi Hasken Rayuwa' na wannan makon tare da Shamsiyya Haruna ya maida hankali ne kan nazarin da masana kimiya suka yi wajen kirkirar Tabaraun hangen nesa, don taimakawa masu raunin gani. A jamhuriyar Nijar, matsalar gani na zama babban kalubale ga al'ummar kasar wacce a yanzu har aka fara samunta a tsakanin matasa. Tuni dai matsalar ta sanya likitoci fara kiraye-kiraye ga al'umma da su tashi tsaye wajen kula da lafiyar idonsu.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin......
-
Iyayen dalibai a Nijar na kokawa kan tsadar kudin karatu
14/11/2023 Duración: 10minShirin 'Ilimi Hasken Rayuwa' na wannan makon tare da Shamsiyya Haruna ya maida hankali ne kan yadda iyaye ke kokawa a jamhuriyar Nijar kan tsadar kudin karatun 'ya'yansu, masamman makaruntu masu zaman kansu saboda matsaloli na tsadar rayuwa da aka shiga tun bayan da sojoji suka yi juyin mulki.
-
Najeriya: Yadda tsadar man fetur ke ci gaba da yin tasiri kan harkar ilimi
31/10/2023 Duración: 10minShirin 'Ilimi Hasken Rayuwa' na wannan mako tare da Shamsiyya Haruna ya maida hankali ne kan yadda matsalar tsadar man fetur ke ci gaba da yin tasiri akan harkar ilimi a Najeriya, wanda tun bayan sanar da janye tallafin mai a kasar kanana da manyan makarantu ke daukan matakai daban daban da zummar daidaita harkokinsu a cikin wannan yanayi. Daga cikin wadannan matakai, wasu manyan makarantun musamman jami'o'i sun takaita ranakun zuwan aikin malamai tare da tsawaita lokutan darrusan dalibai.