Tattaunawa Da Ra'ayin Masu Saurare

Ra'ayoyin Masu Saurare kan zaɓen Faransa

Informações:

Sinopsis

Cikunan ƴan siyasa sun ɗuri ruwa a Faransa, bayan da masu tsattsauran ra’ayi suka lashe sama da 33% na ƙuri’un da aka kaɗa a zaɓen shiga Majalisar Dokokin Ƙasar, tare da yiyuwar samun gagarumar nasara a zagaye na biyu na zaɓen da za a yi ranar Lahadi mai zuwa. Ana matuƙar nuna fargaba dangane da abin da zai faru matuƙar masu wannan ra’ayi suka samu rinjaye a majalisar, saboda tsauraran manufofinsu da suka haɗa da ƙyamar baƙi da kuma neman rage duk wani taimako da ake bai wa ƙasashe masu tasowa.Shin ko yaya kuke kallon wannan lamari da ke faruwa a fagen siyasar ƙasar ta Faransa?Wannan shi ne abin da shirin Ra'ayoyin Masu Saurare na wannan rana ya tattauna a kai.Ku latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyin jama'a.