Tattaunawa Da Ra'ayin Masu Saurare

Ra'ayoyin ƴan Najeriya kan jawabin shugaba Tinubu game da zanga-zanga

Informações:

Sinopsis

Shugaban  Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya buƙaci al’ummar ƙasar su jingine zanga-zanga tare da bayyana aniyar tattaunawa don laluɓo masalaha. A jawabin da ya gabatar sakamakon zanga-zangar tsadar rayuwa da ta ɓarke a akasarin sassan ƙasar, Tinubu ya shaida wa ƴan Najeriya cewa yana jin raɗaɗin da suke ji, kuma tabbas zai samo mafita.Yaya wannan jawabi nasa ya riske ku?Ko ya taɓo batutuwan da suke ci wa al’umma tuwo a ƙwarya?Wace shawara za ku ba wa masu zanga-zanga?