Tattaunawa Da Ra'ayin Masu Saurare

Ra'ayoyin masu saurare kan ambaliyar ruwa a Afrika

Informações:

Sinopsis

Yamai babban birnin Jamhuriyar, ya fara karɓar baƙuncin taron ƙwararru da saurann masu ruwa da tsaki kan matsalar sauyin yanayi da ta shafe yankin yammacin Afrika. Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da sassan yankin na Yammacin Afirka da Sahel ke fuskantar Iftila’in Ambaliyar mafi muni da aka taɓa gani cikin aƙalla shekaru 20, kamar yadda aka gani a garin Maiduguri, inda a baya bayan nan saukar ruwan sama ya janyo tumbatsar dam ɗin da ya fashe, lamarin ya haddasa mummunar ambaliyar da ta mamaye sassan birnin da dama.Wane hali ake ciki a garin na Maiduguri bayan iftila’in da ya auku?Wadanne dabaru ya dace a bi wajen daƙile sake aukuwar haka, ko kuma rage girman barazanar da aka gani, ta hanyar karkatar da tarin ruwan da ke ambaliya zuwa ga amfanin jama’a?Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin